islamkingdomfacebook islamkingdomyoutube islamkingdomtwitte


Addua muhimmancinta da sharadanta


32146
Surantawa
Haqiqa yin addua shi ne tsananta kwadayi ga Allah Taala wajen neman biyan buqatun duniya da na lahira da yaye baqin ciki da kade sharri, da balai na duniya da lahira. Da addua ne bautar Ubangijin talikai takan tabbata, domin ta qunshi ratayuwar zuciya da Allah Taala da Ikhlasi gare shi, da rashin waiwayen wani ba shi ba.

Manufofin huxubar

Bayanin ma’anar addu’a da buqatuwar halitta zuwa gare ta.

Bayanin hukunce-hukuncenta da sharadanta da ladubbanta.

Gargaxi a kan wasu kurakurai dangane da addu’a

Huxuba Ta Farko

Dukkan yabo ya tabbata ga Allah muna yabon Sa muna neman taimakonsa, muna neman gafararsa, muna neman tsarinsa. Duk wanda Allah Ya shiryar babu mai vatar da shi wanda kuma ya vatar babu mai shiryar da shi kuma ina shaidawa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah shi kaxai ba shi da abokin tarayya. Kuma ina shaidawa cewa, Annabi Muhammadu bawansa ne manzonsa ne (ya ku waxanda suka yi imani kuji tsoron Allah yadda ya cancanci a ji tsioronsa, kada ku mutu face kuma musulmi) (ya ku mutane kuji tsoron Ubangijimku wanda ya halicceku daga rai guda xaya, kuma ya halicci matar sa daga gare shi, kuma ya yaxa maza da mata daresu (su biyu) ku ji tsoron allah wanda kuke yi wa junanku magiya dashi (kuma ku kiyaye) zumunci lalle Allah mai kulane daku) (yak ku waxanda kuka yi imani ku ji tsoron Allah kuma ku faxi Magana ta daidai, sai Allah ya gyara muku ayyukanku kuma ya gafarta muku zunubanku, wanda yabi Allaha da Manzon Allah haqiqa ya rabauta rabauta mai girma). Bayan haka, lalle mafi gaskiyar magana maganar Allah, kuma mafi kyawun shiriya shiriyar Annami Muhammad (ﷺ) kumamafi sharin al’amura (a addini) qagaggunsu. Kuma duk wani qagaggen abu (a addini) bidi’a ce, kuma duk warta bidi’a vata ce, kuma duk wani bata yana wuta.

Bayan haka;

Ya ku bayin Allah, ku sani cewa dukkan halitta mabuqata ne zuwa Ubangijinsu wajen janyo musu amfani da ije musu cututtuk, domin gyara addininsu da duniyarsu. Kuma kuma kamalar mutum tana tattare da tabbatar da bautarsa ga Allah mai girma da xaukaka, kuma duk sanda bawa ya qara tabbatar da bautarsa sai kamalarsa ta qaru, kuma darajarsa ta xaukaka, kuma Allah mai girma da xaukaka yana jarrabar bayinsa da wasu abubuwa masu bijirowa da sukan tura su zuwa qofarsa su neman agajjinsa, kuma buqatuwa zuwa ga Allah, ita ce haqiqanin wadatuwarsa. Kuma qaunar bauta da babbar manufarta, da kuma qasqantar da kai ga Allah mai tsarkin mulki shi ne xaukakar da ba za a iya gasa da ita ba. Kuma addu’a ita ce alamar bauta, Allah yana son bayinsa su roqe shi a cikin dukkannin buqatunsu. Domin ya zo cikin Sahih Musulim daga hadisin Abi Zarr, Allah Ya qara yarda a gare shi, Allah Maxaukakin Sarki Ya ce: “Ya ku bayina dukkaninku vatattu ne sai fa wanda na shiryar da shi, to ku nemi shiriyata, zan shiryar da ku. Ya ku bayina dukkanin ku mayunwata ne, sai fa wanda na ciyar da shi, to ku nemi ciyarwata, zan ciyar da ku. Ya ku bayina dukkaninku matsiraita ne, sai fa wanda na tufatar da shi, to ku nemi tufatarwa zan tufatar da ku. Ya ku bayina haqiqa kuna yin kuskure da dare da rana, ni kuma in gafarta zunubi baki xaya, ku nemi gafara ta zan gafarta muku...”.

Ya ku bayin Allah, ku yi sani cewa, Allah (S.W.T) ya hore hanyoyin samun rabo, kuma ya huwace hanyoyin tavewa. Kuma ya jera abubuwa masu faruwa a bisa dalilan faruwarsu, kuma ya halicci sakamakon da za su haifar. Kuma babu wani abu da yake hukunta kansa da nufinsa. Da ya so da ya samar da abu ba tare da sababi ba. Allah Ta’ala Ya ce,

) فَعَّالٌ لِمَا يُرِيدُ16 ( [البروج: ١٦]

(Shi mai aikatawa ne ga abin da ya yi nufi).

Kuma Maxaukakin Sarki ya ce:

(أَلَا لَهُ الْخَلْقُ وَالْأَمْرُ تَبَارَكَ اللَّهُ رَبُّ الْعَالَمِينَ54) [الأعراف: 54]

Ma’ana: (Lalle halitta da umarni na shi ne. Albarkatun Allah sun yawaita. Ubangijin talikai).

Don haka, addu’a dalili ne babba na rabauta da alherai da albarkatai. Kuma dalili ne na na yaye baqin ciki, da sharri da bala’i. Tirmizi ya ruwaito daga Ibn Umar (R.A) ya ce, “Addu’a tana amfani ga abin da ya sauka, da ma wanda bai sauka ba.”

Addu’a tana daga cikin qaddara, kuma sabab ce daga sabubba masu amfani, masu janyo alheri su ije dukkan sharri.

Haqiqa Allah ya yi umarni da addu’a a cinkin ayoyi masu yawa, ya ce,

(وَقَالَ رَبُّكُمُ ادْعُونِي أَسْتَجِبْ لَكُمْ إِنَّ الَّذِينَ يَسْتَكْبِرُونَ عَنْ عِبَادَتِي سَيَدْخُلُونَ جَهَنَّمَ دَاخِرِينَ60) [غافر: 60]

(Kuma Ubangijinka ya ce, ku roqe ni, na amsa muku. Haqiqa waxanda suke girman kai ga barin bautata za su shiga wutar Jahannama suna qasqantattu).

Ya ku bayim Allah! Ku sani cewa haqiqa yin addu’a shi ne: tsananta kwaxayi ga Allah Ta’ala wajen neman biyan buqatun duniya da na lahira da yaye baqin ciki da kaxe sharri, da bala’i na duniya da lahira. Da addu’a ne bautar Ubangijin talikai takan tabbata, domin ta qunshi ratayuwar zuciya da Allah Ta’ala da Ikhlasi gare shi, da rashin waiwayen wani ba shi ba.

Addu’a ta qunshi sakankancewa da cewa Allah mai cikakken iko ne, babu wani abu da zai gajiyar da shi, babu wani abu da zai vuya a gare shi, mai rahama mai jinqai. Rayayye ne, mai isa da zatinsa, ma’abocin alheri har abada, ba a iyakance baiwarsa da alherinsa. Taskokin albarkatunsa ba sa qarewa.

Addu’a ta qunshi buqaturuwar bawa da tsananin matsiwarsa zuwa Ubangijinsa, waxannan abubuwa ne haqiqanin ma’anar ibada.

Ya ku bayin Allah! Haqiqa ximbin nassoshi na hadisazan Annabi sun zo game da falalar addu’a. Daga cikinsu akwai abin da Abu Dawud da Tirmizi suka ruwaito daga Nu’uman bn Bashir, Allah ya qara yarda a gare su daga Annabi (ﷺ) ya ce: “Addu’a ita ce ibada.” Tirmizi ya ce: hadisi ne kyakkyawa ingantacce.

Kuma an karvo daga Abu Hurairah Allah ya qara yarda a gare shi ya ce daga Annabi (ﷺ) ya ce: “Babu wani abu da ya fi girma wajen Allah kamar addu’a.” Ahmad da Tirmizi da Ibn Majah da Ibn Hibbana suka rawaito.

Hakanan ana rawaito daga Abu Hurairah (R.A) ya ce, Manzon Allah (ﷺ) ya ce: "Haqiqa Allah mai girma da buwaya yana cewa: “Ni ina wajan zaton bawana gare ni, kuma ni ina tare da shi (da sani na) idan ya ambace ni”. Bukhari da Muslim ne suka rawaito shi kuma lafazinsa ne. Haka nan Tirmizi da Nisa’i da Ibn Majah duk sun rawaito shi.

An karvo daga Ubadah xan Samit (R.A) cewa, Manzon Allah (ﷺ) ya ce, “Babu wani musulmi a ban qasa da zai roqi Allah da wata addu’a face ya ba shi ita, ko ya kaxe masa wani mummunan abu a madadinta, matuqar ba ya roqi wani abin laifi ba ko yanke zumunci". Sai wani mutum daga cikin mutanen ya ce: "Ashe za mu yawaita ke nan". Sai ya ce: “Allah Shi ne mafi yawaita wa.” Tirmizi ya rawaito kuma ya inganta shi.

Ya ku bayi Allah! Ku sani cewa ba a roqon kowa sai Allah, ba wani mala’ika makusanci ga Allah, ko wani Annabi mursali, ko wani waliyyi nagartacce. Kuma duk wanda ya kirayi wani abin halitta ba Allah ba, Annabi ne ko mala’ika, ko waliyyi, ko aljan, ko kabari, ko makamancinsa, to haqiqa ya yi shirka da Allah Ta’ala, cikin ibadarsa, shirka da za ta fitar da shi daga musulunci. Allah Ta’ala Ya ce:

(وَأَنَّ الْمَسَاجِدَ لِلَّهِ فَلَا تَدْعُوا مَعَ اللَّهِ أَحَدًا18) [الجن: 18]

(Kuma haqiqa masallatai na Allah ne, don haka kada ku kira wani tare da Allah).

Kuma maxaukakin sarki ya ce,

(وَمَنْ يَدْعُ مَعَ اللَّهِ إِلَهًا آَخَرَ لَا بُرْهَانَ لَهُ بِهِ فَإِنَّمَا حِسَابُهُ عِنْدَ رَبِّهِ إِنَّهُ لَا يُفْلِحُ الْكَافِرُونَ117) [المؤمنون: 117]

(Kuma wanda ya kira yi wanin Ubangijin tare da Allah wanda ba shi da wani dalili (ga bauta masa), lallai to wannan hisabinsa yana wajan ubangijinsa, lallai kafirai ba su rabauta ba).

Kuma Ya ce,

(وَلَا تَدْعُ مِنْ دُونِ اللَّهِ مَا لَا يَنْفَعُكَ وَلَا يَضُرُّكَ فَإِنْ فَعَلْتَ فَإِنَّكَ إِذًا مِنَ الظَّالِمِينَ106) [يونس: 106]

(Kada ka kirawo wani ba Allah ba, wanda ba zai amfaneka ba, kuma ba zai cutar da kai ba, idan kuwa ka aikata haka, to lallai kai kana cikin azzalumai). Kuma ya ce,

(الرَّحِيمُ وَإِنْ يَمْسَسْكَ اللَّهُ بِضُرٍّ فَلَا كَاشِفَ لَهُ إِلَّا هُوَ وَإِنْ يُرِدْكَ بِخَيْرٍ فَلَا رَادَّ لِفَضْلِهِ يُصِيبُ بِهِ مَنْ يَشَاءُ مِنْ عِبَادِهِ وَهُوَ الْغَفُورُ107) [يونس: 107]

(Kuma idan Allah ya jarrabe ka da cuta to babu mai yaye maka ita face shi, idan kuma ya nufe ka da alheri to babu mai mai da falalarsa, yana samar wanda ya so daga bayinsa da shi, kuma shi ne mai gafara mai Jinqai).

Kuma Allah Ta’ala Ya ce,

(وَيَوْمَ يَحْشُرُهُمْ جَمِيعًا ثُمَّ يَقُولُ لِلْمَلَائِكَةِ أَهَؤُلَاءِ إِيَّاكُمْ كَانُوا يَعْبُدُونَ40) [سبأ: 40]

(Kuma ranar da zai tashe su gaba xaya sannan ya ce da mala’ikunsa, shin waxannan ku ne suka kasance suna bautawa? Sai su ce tsarki ya tabbata a gare ka, kai ne majivincinmu, ba su ba. Kaxai sun kasance suna bautawa aljannu ne mafi yawancinsu masu ba da gaskiya ne da su.)

Ya ku Musulmi! Haqiqa addu’a tana da lokuta na musamman, kuma aka fi qaunar amsa ta a cikinsu waxanda su ne; addu’a a cikin sujjada. Daga Abu Huraira Allah ya yarda da shi, daga Annabi (ﷺ) ya ce, “Lokacin da bawa ya fi kusa da Ubangijinsa, shi ne lokacin da yake sujjada. Don haka, ku yawaita addu’a a cikinta.” Muslim ne ya rawaito shi.

Kuma an karvo daga Ibn Abbas (R.A.), ya ce: MAnzon Allah (ﷺ) ya ce: “Lalle haqiqa ni an hana ni in karanta Alqur’ani a cikin ruku’u ko sujjada. Amma ruku’u to ku girmama Ubanjigi a cikinsa. Ita kuma sujjada, to ku yi matuqar qoqari wajen addu’a a cikinta, lallai ya dace amsa muku.” Muslim ne ya rawaito shi.

Daga ciki: akwai tsakanin kiran sallah da iqama. Domin an rawaito daga Anas (R.A) ya ce: Manzon Allah (ﷺ) ya ce: “Ba a mayar da addu’a a tsakanin kiran sallah da iqama.” Tirmizi ne ya fitar da shi, kuma ya ce, hadisi ne kyakkyawa ingantacce.

Kuma gada ciki: akwai yayin da sulusin dare na qarshe ya rage. Domin ya zo a cikin sahihin Bukhari, Manzon Allah, tsira da aminci su tabbata a gare shi ya ce: “Ubangijinmu kan sauka (irin saukar da ta dace da shi), kowane dare zuwa saman duniya yayin da sulusin dare na qarshe ya rage, sai ya ce “Wane ne zai kira ni na amsa masa? Wane ne zai nemi gafara ta na gafarta masa?”.

Daga ciki: akwai qarshen sa'a bayan sallar La’asar ranar juma’a. An rawaito daga Abi Huraira (R.A) cewa Manzon Allah (ﷺ) ya ambaci ranar Juma’a sai ya ce “A cikinta akwai wata sa'a babu wani bawa Musulmi da zai dace da ita a tsaye yana sallah, yana roqon Allah wani abu face ya ba shi. Ya yi nuni da hannunsa yana qarantata.” Bukhtari da Muslim ne suka rawaito shi.

Ma’abota ilimi suna da mazhabobi da dama wajen tantance wannan sa'ar ta ranar Juma’a. Amma mafi inganci shi ne cewa, qarshen sa'a bayan La’asar, kamar yadda yake a cikin hadisin Abi Dawud da waninsa, Annabi (ﷺ) ya ce, (Ranar Juma’a sa'a sha biyu ce, ba za a samun wani Musulmi yana roqon Allah wani abu a cikinta face ya ba shi. Ku neme ta a sa'a ta qarshe bayan sallar La’asar).

Yana daga guraren amsa addu’a da shari’a ta zo da su: Daren Lailatul Qadari, da ranar Arafa, da gurin Hajarul Aswad, da yayin saukar ruwan sama, da bayan sallolin farilla, da lokacin shan ruwa a yayin azumi.

Ya ku bayin Allah! Ku ganimanci falalar Ubangijinku, ku fake zuwa gare shi cikin lamuranku. Ku xaukaka tafukanku da qasqan da kai, ko a amsa addu’o’inku! Kuma ku rabauta da yardar Ubangijinku.

Ina faxar abin da kuke ji kuma ina neman gafarar Allah Maxaukakin Mai girma ga kaina da ku, da a kuma sauran Musulmi daga kowane zunubi. Lallai shi ne Mai yawan gafara Mai yawan jinqai.

Godiya ta tabbata ga Allah wannan da ya shiryar da majivintansa ga addinin musulunci, ina yabansa ina gode masa a bisa datarwarsa da shiyarwarsa, ina shaidawa cewa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah shi kaxai, ba shi da abokin tarayya ma’abocin buwaya da girma. Kuma ina shaidawa cewa Annabu Muhammad Manzon Allah ne amintacce. Allah ka yi salati da sallama a bisa bawanka da kuma manzonka Muhammadu da alayansa, da sahabansa gabaxaya.

Ku sani ya ku bayin Allah cewa, addu’a tana da sharuxxa waxanda dole sai an cika su kafin addu’ar bawa ta samu karvuwa wajen Ubangijin sa, su ne kamar haka;

Na farko: Tsarkake tauhidi ga Allah Ta’ala. Allah Ya ce:

(فَادْعُوا اللَّهَ مُخْلِصِينَ لَهُ الدِّينَ وَلَوْ كَرِهَ الْكَافِرُونَ14) [غافر: 14]

(Don haka ku kira Allah kuna masu tsarkake addini a gare shi, ko da kafirai sun qi). Kuma haqiqa ya zo a cikin hadisil Qudusi: “Ya kai xan’adam haqiqa kai da za ka zo mini da cikin qasa na zunubai, sannan ka gamu da ni ba ka tara bauta ta da wani abu ba, da na zo maka da kwatankwacinta na gafara.” Tirmizi ne ya rawaito shi.

Na biyu: Nisantar haram a cimarka, da abin sha da tufafi; domin Muslim ya rawaito a cikin sahihinsa, daga hadisin Abu Huraira (R.A) cewa, Manzon Allah (ﷺ) ya ce “Ya ku mutane haqiqa Allah Ta’ala tsarkakakke ne, ba ya karva sai tsarkakkake. Kuma Allah ya umarci Muminai da abin da ya umarci Manzanni da shi, sai ya ce,

(يَا أَيُّهَا الرُّسُلُ كُلُوا مِنَ الطَّيِّبَاتِ وَاعْمَلُوا صَالِحًا إِنِّي بِمَا تَعْمَلُونَ عَلِيمٌ51) [المؤمنون: 51]

(Ya ku manzanni ku ci daga daxaxa, kuma ku aikata aiki na gari, haqiqa Ni masani ne da abin da kuke aikatawa). kuma ya ce,

(يَا أَيُّهَا الَّذِينَ آَمَنُوا كُلُوا مِنْ طَيِّبَاتِ مَا رَزَقْنَاكُمْ وَاشْكُرُوا لِلَّهِ إِنْ كُنْتُمْ إِيَّاهُ تَعْبُدُونَ172) [البقرة: 172] (Ya ku waxanda suka yi imani, ku ci daga daxaxan abin da muka azurta ku, kuma ku yi godiya ga Allah in kun kasance shi kaxai kuke bautawa).

Sannan ya ambaci mutum da yake tsawaita tafiya, mai hargitsattsan gashi, mai buxu-buxu, yana xaga hannayensa zuwa sama, (yana addu’a yana mai cewa): Ya Ubangiji! Ya Ubangiji!! (Alhali) abincinsa haramun ne, abin shansa haramun ne, kuma tufafinsa haramun ne, kuma an ciyar da shi da haramu, to ta yaya za a amsa masa.”

Na uku: halartowar zucitya da qarfin fata, domin an rawaito daga Abu Huraira (R.A) daga Annabi (ﷺ) ya ce: “Ku roqi Allah, kuna masu sakankancewa da amsawa, kuma ku sani cewa Allah baya qarvar addu’a daga zuciya gafalalliya mai wasa”. Tirmizi ne ya rawaito shi.

Na Huxu: ya gabatar da yabo ga Allah da salati ga Annabi (ﷺ) gabannin gabatar da buqatarsa, sabda abin da ya zo a cikin ingatatcciyar sunna game da haka.

Kamar yadda addu’a ta ke da wasu ladabbai da ya kamata bawa ya lura da su yayin da yake yin addu’a.

Daga waxannan ladubba akwai:

Ya kasance cikin tsarki, domin addu’a zikiri ce, gashi kuma hadisi ya inganta daga Annabi (ﷺ) cewa, ya yi taimama daga garun wani bango domin amsa sallama, sannan ya ce “Na qyamaci na ambaci Allah ba tare da ina cikin tsarki ba” Abu Dawud ne ya fitar da shi.

Xaga hannaye, saboda abin da ya zo a cikin hadisi “Haqiqa Ubangijinku mai kunya ne, mai karamci ne, yana jin kunyar bayinsa idan suka xaga hannayensu zuwa gare shi, su mai da su fayau.” Hakim ne ya fitar da shi, kuma ya inganta shi. Kuma Azzahabi ya goyi bayansa.

Ya qarfafa aniyarsa a kan addu’ar, saboda faxin Annabi (ﷺ): “Idan xayanku zai yi addu’a to ya qarfafa aniyarsa, kada ya ce "Ya Ubangiji to idan ka so ka ba ni", domin ba mai tilasta masa” Bukhari ne ya fitar da shi.

Ya kirdadi sigogin addu’a da aka rawaito musamman waxanda suka zo cewa sun qunshi Ismul A’azam, domin ya zo a cikin sahihin Ibn Hibbana daga hadisin Abdullahi bn Buraidah daga babansa (R.A.) cewa, Manzon Allah (ﷺ) ya ji wani mutum yana cewa “Ya Ubangiji ni ina roqonka da cewa ni ina shaidawa kai kaxai ne Allah, babu abin bautawa da gaskiya sai kai. Kai kaxai ne abin nufi da buqata, wanda bai haifa ba, ba a haife shi ba, kuma babu wani da ya kasance tamka a gare shi”, Sai ya ce, “Haqiqa in an tambaye Shi da shi yana bayarwa, kuma idan an roke shi da shi, sai ya amsa”. A wani lafazin “Haqiqa ka tambayi Allah da sunansa mafi girma.” Hadisi ne ingantacce. A cikin sunana daga hadisin Anas xan Malik (R.A) cewa, shi ya kasance tare da Manzon Allah (ﷺ) yana zaune, wani sai ya ce, “Ya Ubangiji, ni ina roqon ka da cewa yabo ya tabbata a gare ka, babu abin bautawa da gaskiya sai kai, Mai baiwa, maqagin sammai da qassai, ya ma’abocin buwaya da girmamawa ya rayayye, ya tsayayye (da lamuran halitta).” Sai Annabi (ﷺ) ya ce, “Haqiqa ya kira Allah da sunansa mai girma, wanda idan an roke shi da shi yake amsawa, kuma idan an tambaye shi da shi yake bayarwa”. (hadisi ne ingantace).

Kuma Bukhari da Muslim sun ruwai daga Ibn Abbas, cewa Manzon Allah (ﷺ) ya kasance yana faxa yayin baqin ciki “Babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, Ubangijin Al’arshi mai girma, babu abin bautawa da gaskiya sai Allah Ubangijin sammai da qassai, Ubangijin al’arshi mai karamci".,

Ya ku bayin Allah! Ya wajaba mu dauwama kan addu’o’i. Ba wai loakcin da musubu da bala'i suka afko ba kaxai, sai dai kamar yadda ya zo a cikin hadisin Annabi wanda Abu Hurairah (R.A) ya rawaito daga gare shi mai tsira da amincin Allah, ya ce, “Wanda ya ke son Allah ya karva addu'arsa a lokacin tsanani, to ya yawaita addu’a yayin da yake cikin yalwa.” Tirmizi ne ya rawaito, kuma Hakim ya inganta shi.

Allah yana cewa,

(أَمَّنْ يُجِيبُ الْمُضْطَرَّ إِذَا دَعَاهُ وَيَكْشِفُ السُّوءَ وَيَجْعَلُكُمْ خُلَفَاءَ الْأَرْضِ أَئِلَهٌ مَعَ اللَّهِ قَلِيلًا مَا تَذَكَّرُونَ62) [النمل: 62]

(Shin wanene wanda yake amsawa mabuqaci yayin da ya kira shi, kuma yake yaye cuta, kuma yake sanya halifofi a qasa. Shin akwai wani abin bauta tare da Allah. Kaxanne kwarai kuke wa’azantuwa). .

Kuma Allah Ta’ala Ya ce,

(وَإِذَا سَأَلَكَ عِبَادِي عَنِّي فَإِنِّي قَرِيبٌ أُجِيبُ دَعْوَةَ الدَّاعِ إِذَا دَعَانِ فَلْيَسْتَجِيبُوا لِي وَلْيُؤْمِنُوا بِي لَعَلَّهُمْ يَرْشُدُونَ186) [البقرة: 186]

(Kuma yayin da bayina suka yambayeka game da ni, to ni makusanci ne, ina amsa addu’ar mai addu’a idan ya kirani).

Ina addu’o’in da muke yi kafin salloli, da cikin salloli, da bayan salloli? Ina addu’o’inmu a tarurruka, Ina addu’o’in da muke yi a ciki sirri da kevancewa da tsakiyar dare da gabanin alfijiri da cikin awoyin qarshen na dare, da ranakun masifa, ko lokacin bala’i? A koyaushe, to ina gafallalu? Mu kuwa – in banda waxanda Allah ya jiqansu – muna cikinsu. Ina masu addu’a masu qasqantar da kai, mu ga yaya sakankacewarsu da wannan addu’a, ranar da imani yake kafe a cikin zuqata, ranar da nagarta da istiqama suke bayyane cikin voyayyun halaye da bayyanannunsu. Xayansu ya kasance yana addu’a yana mai yankewa da sakankancewa da amsawar Allah ga wannan addu’a. Har wasu suka shahara tsakanin sahabbai - Allah ya yarda da su - a kan cewa su, ababen amsa addu’ar su ne, kamar yadda ya ke a qissar Sa’ad xan Abu Waqqas.

Ga dai Sa’id ibn Zaid, xaya daga goma waxanda aka yi musu bushara da aljanna. Wata mata ta yi da’awa da qage cewa ya qwace mata wani yanki na qasarta, yayin da aka yi masa magana kan haka, sai ya ce “Yaya haka, alhali ni na ji cewa, wanda ya qwaci taku xaya na qasa ba tare da haqqinsa ba, to za a rataya masa shi tun daga qasan-bakwai ranar alqiyama”. Sannan ya ce, “Ya Ubangiji idan qarya take, to ka makantar da ita, kuma ka sanya qabarinta a cikin gidanta. Sai ta makance, kuma ta faxa wata rijiyarta a cikin gidanta ta mutu.

Hakanan Abu Mu’awiya Al’aswad a lokacin gwabzawa da Rumawa, wani kafiri daga kafiransu ya fito. Wanda cutarsa to tsananta ga Musulmi, sai wani daga cikin musulmi ya zo masa (shi Mu’awiya) sai ya ce “Wannan ya aikata kaza da kaza, ka roqi Allah a kansa». Sai ya xauki mashinsa ya yi addu’a ya ce, “Kuma ba ka yi jifa ba yayin da ka yi jifa sai dai Allah shi ne ya yi jifa”. Sannan ya ce “Ina kuke so? Suka ce “Mazakutarsa” Sai suka jefa shi, kuma ba su kuskure gurin da suka faxa ba. Sai ya kashe maqiyin Allah (S.W.T).

Wasu mutane ba su gushe ba suna cewa, “Mun yi ta yin addu’a amma ba a amsa mana ba. Don haka mu ba mu ga amfaninta ba». Alhali ba su san cewa su ne ba su cika sharuxxan amsa addu’ar ba. Kuma su sun vata hanyar addu’ar, da kavar addu’ar zuwa ga Allah Mai Buwaya da xaukaka, saboda raunin yaqini da raunin imani, baya ga kau da kai ga barin biyayya da afkawa cikin savo.

Ya ku bayin Allah! Ya wajaba musan haqiqanin addu’a da muhimmancinta da girmanta a cikin wannan addinin kuma cewa, ita alama ce ta kamalar bautar bawa ga Ubangijinsa, kuma mu lazimci hanya madaidaciyya cikin addu’armu. Mu koyi sonnonin Annabi da ladubban shari’a a cikinta, in mun yi haka Allah zai sanya mu cikin waxanda ake amsa addu’o’in su ya karvi qasqan da kanmu, da aikinmu. Lallai Shi ne mai amsawa, kuma mai cancanta ne da amsawa. Allah Ya yi tsira da aminci a bisa Annabi Muhammadu da alayensa da sahabansa baki xaya.