islamkingdomfacebook islamkingdomyoutube islamkingdomtwitte


Zakka da gudumawar da take bayarwa wajen taimakon aluma


6624
Surantawa
waye a cikinmu baya son a qara masa arziqinsa, dukiyarsa ta qaru? Allah ya tsarkake masa ita, ya yi masa albarka a cikinta? To ku taho zuwa ga abin yake sanya haka, wannan abu ba komai ba ne face bayar da zakka.
huxuba ta

Manufofin huxubar

Bayanin wajabcin bayar da zakka, da irin dukiyoyin da ake bada zakka a cikinsu.

Bayanin ta’asirin zakka a cikin al’umma.

Tsoratarwa daga hana zakka.

Bayanin hikomomin wajabta bayar da zakka.

Huxuba Ta Farko

Dukkan yabo da godiya da kirari sun tabbata ga Allah, taimakonsa da gafararsa muke nema, kuma muna neman tsarinsa daga shirrin kawukanmu da munanan ayyukanmu. Wanda Allah ya shiryar babu mai vatar da shi, wanda kuma ya vatar to babu mai shiryar da shi. Kuma ina shaidawa babu abin bauta da gaskiya sai Allah, shi kaxai ne ba shi da abokin tarayya. Kuma ina shaidawa cewa, Annabi Muhammad bawansa ne manzonsa ne. (Ya ku waxanda suka yi imani ku ji tsoron yadda ya cancaci a ji tsoronsa, kada ku mutu face kuna musulmi). (Ya ku mutane ku ji tsoron Ubangijinku wanda ya halicceku daga rai guda xaya, kuma ya ya halicci matarsa daga gare shi, kuma ya yaxa maza da mata daga garesu (su biyu). Ku ji tsoron Allah wanda kuke yiwa junanku magiya da shi, (kuma ku kiyaye) zumunci. Lalle Allah mai kula ne da ku). (Ya ku wanxanda suka yi imani ku ku ji tsoron Allah kuma ku faxi magana ta daidai. Sai Allah ya gyara muku ayyukanku, kuma ya gafarta muku zunubbanku. Wanda ya bi Allah da Manzonsa haqiqa ya rabauta rabauta mai girma). Bayan haka, lalle mafi gaskiyar magana maganar Allah, kuma mafi kyawon shiriya shiriyar Annab Muhammad (ﷺ). Kuma mafi shirrin al'amura (a addini) qagaggunsu, kuma duk wani qagaggen abu (addini) bidi'a ce, duk wata bidi'a vata ce, duka wani vata kuma yana wuta.

Bayin Allah : waye a cikinmu baya son a qara masa arziqinsa, dukiyarsa ta qaru? Allah ya tsarkake masa ita, ya yi masa albarka a cikinta? To ku taho zuwa ga abin yake sanya haka, wannan abu ba komai ba ne face bayar da zakka. Wannan ibadar ta dukiya da Allah Maxaukakin Sarki ya wajabta ta akan bayinsa, don haka – Yaku bayin Allah – ku bayar da abin da Allah ya wajabta muku a cikin dukiyoyinku, wadda Allah ya azurta da ita, haqiqa ya fitar da ku daga cikin iyayenku baku da komai, baku san komai ba, ba kwa mallakar amfani ko cutarwa ga kawunanku, sannan ya azurta ku, ya baku abin da baku tava tunanin samunsa ba, don haka ku gode masa, ku bayar da abin da ya wajabta muku, don ku samu kuvuta, kuma dukiyoyinku su tsarkaka. Ku nisanci rowa da son kai da abin da Allah ya wajabta muku, saboda hakan halaka ne, kuma zare albarkar dukiyarku ne. Ku saurara mafi girman abin da Allah ya wajabta muku a cikin dukiyoyinku shi ne bayar da zakka, wadda take rukuni ne na uku a musulunci, kuma abokiyar haxin sallah ce a cikin Alkur’ani. Sannan ta wajaba akan dukkan musulmi baligi xa, mai hankali, wanda ya mallaki abin da ya kai zakka cikakkiyar mallaka.

Allah Maxaukakin Sarki ya wajabta ta a cikin littafinsa mai girma, inda yake cewa :

( وَأَقِيمُوا الصَّلَاةَ وَآَتُوا الزَّكَاةَ وَارْكَعُوا مَعَ الرَّاكِعِينَ 43 ) [البقرة: 43]

Ma’ana : «Ku tsayar da sallah ku bayar da zakka ku yi ruku’u da masu ruku’u» (Al- Baqara 43).

Ya sake cewa :

( وَأَقِيمُوا الصَّلَاةَ وَآَتُوا الزَّكَاةَ ) [البقرة: 110] .

Ma’ana : “Ku tsaida sallah ku bayar da zakka” (Al-baqra : 110). Haka umarni da bayar da zakka da yin sallah ya yi ta maimaituwa a cikin Alqur’ani har sama da aya (80).

Hakanan Manzon Allah (ﷺ) ya bayyana wa al’ummarsa wajabcinta. An karvo daga Abdullahi xan Umar – Allah ya yarda da shi – ya ce, Manzon Allah (ﷺ) ya ce, “An gina musulunci a bisa abubuwa biyar, akan a kaxaita Allah, da tsaida sallah, da bayar da zakka, da azumin watan Ramadan, da hajji” Bukhari da Muslim ne suka rawaito.

Lamarin zakka bai tsaya nan ba, sai da Allah Maxaukakin Sarki ya yi kashedi mai tsanani akan duk wanda yake hana zakka, Allah ya ce:

( وَلَا يَحْسَبَنَّ الَّذِينَ يَبْخَلُونَ بِمَا آَتَاهُمُ اللَّهُ مِنْ فَضْلِهِ هُوَ خَيْرًا لَهُمْ بَلْ هُوَ شَرٌّ لَهُمْ سَيُطَوَّقُونَ مَا بَخِلُوا بِهِ يَوْمَ الْقِيَامَةِ وَلِلَّهِ مِيرَاثُ السَّمَاوَاتِ وَالْأَرْضِ وَاللَّهُ بِمَا تَعْمَلُونَ خَبِيرٌ 180 ) [آل عمران: 180]

Ma’ana : “kada waxanda suke rowa da abin da Allah ya basu na falalarshi su yi zaton haka alheri ne garesu, a’a hakan sharri ne a garesu, za a naxa musu abin da suka yi rowa da shi ranar alqiyama. Gadon sammai da qassai duk mallakar Allah ne. kuma Allah masani ne dangane da abin da kuke aikatawa”. (Al –Imran : 180).

Ya sake cewa a wurin :

( وَالَّذِينَ يَكْنِزُونَ الذَّهَبَ وَالْفِضَّةَ وَلَا يُنْفِقُونَهَا فِي سَبِيلِ اللَّهِ فَبَشِّرْهُمْ بِعَذَابٍ أَلِيمٍ 34 ) [التوبة: 34]

Ma’ana : «Waxanda suke taskake zinare da azurfa ba sa ciyar da su saboda Allah, ka yi musu bushara da azaba mai tsanani. Ranar da xumama musu ita a cikin wutar Jahannama, a naxe goshinsu da gefensu da bayansu da ita, a ce musu wannan shi ne abin da kuka taskake wa kawunanku, ku xanxani abin da kuke taskakewa». (Attauba )

Manzon Allah (ﷺ) ya fassara ayar farko da faxinsa : “Duk wanda Allah ya bashi dukiya, amma bai bayar da zakkarta ba, za a mayar masa da wannan dukiya ta zama maciji, wanda baya da gashi a kansa saboda yawan dafinsa, a rataya masa shi, yana cafkar muqamuqinsa, yana cewa : “Ni ne dukiyarka, ni ne abin da ka taskake” Bukhari ne ya rawaito.

Yaku musulmi : Ku sani cewa zakka tana da fa’idoji a addinance da xabi’ance cikin al’umma masu yawa, ga kaxan daga cikinsu :

Bayar da zakka tsaida xaya daga cikin rukunan addinin musulunci ne, wanda a kansu arziqin bawa yake duniya da lahira.

Yin zakka yana kusantar da bawa ga Ubangijinsa, kuma tana qara imani, kamar yadda sauran ibadu suke kusantar da bawa ga Allah.

Abin da yake biyo bayan bayar da zakka na lada mai yawa, Allah yana cewa :

( يَمْحَقُ اللَّهُ الرِّبَا وَيُرْبِي الصَّدَقَاتِ ) [البقرة: 276]

“Allah yana shafe albarkar riba, yana renon sadaka” (Albaqra : 276). A wani wurin ya ce,

( وَمَا آَتَيْتُمْ مِنْ رِبًا لِيَرْبُوَ فِي أَمْوَالِ النَّاسِ فَلَا يَرْبُو عِنْدَ اللَّهِ وَمَا آَتَيْتُمْ مِنْ زَكَاةٍ تُرِيدُونَ وَجْهَ اللَّهِ فَأُولَئِكَ هُمُ الْمُضْعِفُونَ 39 ) [الروم: 39]

“Duk abin da kuka bayar na haramun don ya qaru a dukiyar mutane, to ba zai qaru a wurin Allah ba, abin da kuka bayar na sadaka kuna nemar yardar Allah to wannan shi ne mai ninkuwa” (Arrum : 39).

Manzon Allah (ﷺ) ya ce, “Wanda ya yi sadaka da kwatankwacin dabino, daga tsakaken abin ya samu – Allah ba ya karva abu sai mai tsarki – to Allah yana karvar wannan sadakar da hannun damansa, ya reneta kamar yadda xayanku yake renon xan goxiyarsa, har ta zama kamar girman dutse”. Bukhari da Muslim ne suka rawaito.

Allah yana kankare zunubai da ita, kamar yadda Manzon Allah (ﷺ) yake cewa “Sadaka tana kankare zunubai kamar yadda ruwa yake bice wuta”. Anan ana nufin sadakar nafila da ta farilla (zakka).

Daga cikin fa’idojin zakka na gyaran halaye da take kawo wa, akwai :

Zakka tana sanya mai yinta ya zama mai karamci da kyauta da rangwame.

Zakka ta kan sa mai yin ta, ya zama mai tausayi da jin qai ga ‘yan uwansa miskinai. Masu jinqai kuwa Allah mai rahama yana jin qansu.

Abu ne wanda ake gani bada dukiya da jiki ya kan kawo yalwar qirji, da buxewar zuciya, da nutsuwa, kuma yana sanya mutum ya zama abin qauna a wurin ‘yan uwansa musulmai saboda irin amfanin da yake yi wa ‘yan uwansa.

Zakka tana tsarkake mai yin ta daga rowa da son kai, kamar yadda Allah ya ce,

( خُذْ مِنْ أَمْوَالِهِمْ صَدَقَةً تُطَهِّرُهُمْ وَتُزَكِّيهِمْ بِهَا وَصَلِّ عَلَيْهِمْ إِنَّ صَلَاتَكَ سَكَنٌ لَهُمْ وَاللَّهُ سَمِيعٌ عَلِيمٌ 103 ) [التوبة: 103]

«Ka karvi sadaka daga dukiyoyinsu wadda zaka tsarkake su ka gyara su da ita».

A Bangaren zamantakewa kuwa, Zakka tana bada gudummawa mai yawa daga ciki akwai:

A cikinta akwai kawar wa talakawa buqatunsu, waxanda su suka fi yawa a cikin mafi yawan garuruwa.

A cikin zakka akwai qarfafa musulmi, da xaukaka su, don haka ya halatta a bada zakka don yin jihadi saboda Allah.

Zakka tana kawar da gaba da hassada da qyashi da suke cikin zukatan talakawa da miskinai, saboda idan talakawa na ganin masu hali da dukiya suna walwala a cikin dukiyarsu, kuma ba sa amfanarsu da ita, da kaxan koda da yawa, to wannan zai iya jawo gaba da qulli ga mawadata, saboda basu kiyaye haqqinsu ba, ba su biya musu buqatunsu ba. Amma ida mawadata suka bada wani ‘yanki na dukiyarsu ga talakawa a farkon shekara, sai waxannan abubuwa su gushe, a samu soyayya da haxuwa da juna.

A cikin zakka akwai qaruwar dukiya da yawaita albarkarta, kamar yadda hadisi ya nuna.

A cikin zakka akwai faxaxa dukiya da yaxata, saboda dukiya idan aka sarrafa wani abu daga cikinta, sai ta qara buxewa, mutane da yawa su amfanu da ita, savanin idan ta zama tana jujjuyawa tsakanin mawadata kaxai, talakawa ba sa samun komai.

Waxannan fa’idoji gaba xaya suna cikin zakka, kuma suna nuna zakka wani abu ne da yake lallai a same shi don gyara xaixaikun mutane da al’umma. Tsarki ya tabbata ga Allah Masani Mai hikima.

‘Yan uwa muslmi : ku sani zakka tana wajaba ne a cikin wasu abubuwa kevantattu kamar haka :

Kayan da aka tanda don kasuwanci, gidaje ne ko motoci ko dabbobi ko wasu tufafi da sauran nau’ikan dukiya, abin da za a bayar na wajibi a ciki shi ne za a kasa dukiyar goma, a xau kashi xaya a kasa shi huxu sai a bada kashi xaya, Mai kayan zai qimanta shi a farkon kowace shekara ya bada abin da ya cancanta. Amma abin da ya tanada don buqatarsa, ko don yin haya da shi, daga gidaje ko motoci da sauran abin da aka tanada, to babu zakka a cikinsa, saboda Manzon Allah (ﷺ) yana cewa : “Babu zakka akan musulmi cikin bayinsa da dokinsa (abin hawansa)”. Imam Ahmad ne ya rawaito shi.

Abu na biyu da ake fitar wa da zakka shi ne zinare da azurfa ko abin da yake a matsayinsu wajen zama kuxin abubuwa, idan mutum ya mallaki nisabi, kuma shekara ta zagayo a kansa bai ragu ba, to wajibi ne ya lissafa abin da yake da shi ya kasa arba’in ya bada kaso xaya.

Abu na uku da ake fitarwa da zakka : kayan gona, duk wanda ya noma abin da ake ci kuma ana iya ajiye shi, sannan ya kai wisqi sittin, to wajibi ne ya bada zakkarsa anan take.

Waxannan su ne abubuwan da ake fitar wa da zakka, koma bayansu na abin da mutum ya mallaka, na kayan amfanin yau da kullum, kamar motar da yake hawa, ko tufafin da yake sanyawa, da makamantansu to babu zakka a cikinsu.

Yaku bayin Allah : Musulmi nagari shi ne wanda yake kallon dukiyar da Allah ya bashi a matsayin amana, da Allah ya bashi, ya kuma dace ya bada haqqinta, ya yi amfani da ita cikin abin da Allah ya yarda da shi. Ba musulmi nagari ba ne wanda yake xaukar dukiyarsa a matsayin wani abu nashi na dole da ya wajaba Allah ya bashi, kuma yake mata kallon dauwama da rashin qarewa, haqiqa duk wanda ya zama haka to ya yi hasara duniya da lahira. Muna roqon Allah ya kare mu.

Allah ya yi mana albarka cikin abin da muka ji, daga Alqur’ani da Sunnah, ya yi mana gafara, haqiqa shi mai iko ne akan komai.

huxuba ta biyu

Huxuba Ta Biyu

Godiya ta tabbata ga Allah, Kyakkyawan qarshe yana ga masu tsoron Allah, Tsira da Aminci su tabbata ga fiyayyen halitta, Manzon Allah (ﷺ) da iyalansa da Sahabbansa da waxanda suka bi su gaba xayansu, har zuwa ranar sakamako. Bayan haka:

Ya ‘yan uwa : Allah Maxaukakin Sarki ya jivinci bayanin waxanda za a bawa zakka a cikin Alqur’ani mai girma, inda yake cewa :

( إِنَّمَا الصَّدَقَاتُ لِلْفُقَرَاءِ وَالْمَسَاكِينِ وَالْعَامِلِينَ عَلَيْهَا وَالْمُؤَلَّفَةِ قُلُوبُهُمْ وَفِي الرِّقَابِ وَالْغَارِمِينَ وَفِي سَبِيلِ اللَّهِ وَاِبْنِ السَّبِيلِ فَرِيضَةً مِنَ اللَّهِ وَاللَّهُ عَلِيمٌ حَكِيمٌ 60 ) [التوبة: 60]

Ma’ana : «Kaxai sadaka (wato zakka, haqqi ne na) faqirai da miskinai da masu aiki a kanta, da waxanda ake janyo zukatansu, da bayi, da waxanda ake bi bashi, da kuma saboda Allah da matafiya, wajibi ne daga wajen Allah, Allah masani ne mai hikima» (Attauba : 60).

Waxannan sune sinfi takwas da ake bawa zakka : ga bayaninsu xaya bayan xaya :

Faqirai, su ne waxanda ba sa samun abin da zai ishe su, sai xan kaxan wanda bai kai rabi ba, idan ya zama mutum bai mallaki abin da zai iya ciyar da iyalisa ba na wata shida to shi faqiri ne, ya halatta a bashi abin da zai ishe shi da iyalansa tsawon shekara.

Miskinai : su ne waxanda suke da rabin abin da zai ishe su, ko fiye da rabin, amma ba su da abin da zai ishe su shekara guda, don haka sai a cika musu na shekara guda.

Masu aiki a kan zakkar : su ne waxanda shugaba yake wakilta wa don karvo zakkar daga mawadata, sannan su raba ta ga waxanda suka cancanta, su kiyayeta, To waxannan ya halatta a basu zakka gwargwadon aikinsu koda kuwa suna da watada da hali.

Waxanda ake son a ja zukatansu zuwa ga musulunci : su ne shugabannin qabilu, waxanda imaninsu bai yi qarfi ba, ya halatta a basu zakka don qarfafa musu imaninsu, su zama masu kira zuwa ga addinin Allah. Idan mutum yana da raunin imani kuma baya cikin shugabannin da ake yi wa biyayya, kawai yana cikin gama – garin mutane, to shin za a bahi zakka don qarfafa imaninsa, ko kuwa? malamai sun yi savani wajen ba shi zakka!?.

Bayi : wannan ya haxa da sayen bayi da ‘yanta su da kuxin zakka, da fanso ribatattun musulmi daga wurin kafirai, dak da kuxin zakka.

Waxanda ake bi bashi : idan ba su abin da zasu biya bashinsu da shi, to irin waxannan ya halatta a basu abin da zasu biya bashinsu da shi, bashin mai yawa ne ko kaxan, ko da kuwa suna da wadatar abin za su ci, misali da za a qaddara cewa ga wani mutum yana da inda yake samun abincinsa da na iyalansa, amma ana bin shi bashi wanda ba zai iya biya ba, to za a bashi abin zai biya masa bashinsa daga cikin zakka. Ba ya halatta wanda yake bin wani bashi ya sauke masa bashin da abin da ya yi niyya na zakka.

Wajen xaukaka kalmar Allah : wato jihadi don xaukaka kalmar Allah, za baiwa masu jihadi abin da zai ishe su daga zakka don fita zuwa jihadi, a sayi kayan jihadi daga cikin kuxin zakka. Yana cikin Fisabilillahi neman ilimin addini, za a bawa xalibin da yake neman ilimin addini abin da zai iya neman ilimi da shi, daga littattafai da makamantansu, sai dai idan yana dukiyar da zai iya samun abin da yake so.

Matafiyi : shi ne wanda guzuri ya yanke masa, sai a bashi abin da zai kai shi gida daga cikin zakka.

Waxannan su ne waxanda Allah ya ambata a cikin littafinsa, ya kuma bawa waxannan wajibi ne da ya fito daga gare shi a kan ilimi da hikima. Allah Masani ne mai hikima.

Ba ya halatta a sarrafa zakka a cikin waxanda ba waxannan ba, kamar gina masallaci, ko gyara hanya, saboda Allah ya faxi waxanda suka cancanci zakka a keve, keve abu kuwa yana kore shi daga wanda ba shi ba.

Ku ji tsoron Allah – Yaku bayin Allah – ku yi wa kanku hisabi, ku yi adalci, kada ku zaton zakka tara ce ko hasara ce a kanku, a’a wallahi zakka ganima ce da riba ga wanda ya yi ta, kuma xaya ce daga cikin rukunan musulunci, abokiyar sallah ce a cikin littafin Allah. Aiki da ita aiki ne da rukuni mai girma daga rukunan musulunci, sannan tsarki ce daga savo da zunubi ga wanda ya bayar da ita, tsarkake wa ce garehi da ayyukansa, kuma albarka ce da qaruwa a cikin dukiyarsa.

Allah Maxaukakin Sarki ya ce :

( يَا أَيُّهَا الَّذِينَ آَمَنُوا أَنْفِقُوا مِنْ طَيِّبَاتِ مَا كَسَبْتُمْ وَمِمَّا أَخْرَجْنَا لَكُمْ مِنَ الْأَرْضِ وَلَا تَيَمَّمُوا الْخَبِيثَ مِنْهُ تُنْفِقُونَ وَلَسْتُمْ بِآَخِذِيهِ إِلَّا أَنْ تُغْمِضُوا فِيهِ وَاعْلَمُوا أَنَّ اللَّهَ غَنِيٌّ267 الشَّيْطَانُ يَعِدُكُمُ الْفَقْرَ وَيَأْمُرُكُمْ بِالْفَحْشَاءِ وَاللَّهُ يَعِدُكُمْ مَغْفِرَةً مِنْهُ وَفَضْلًا وَاللَّهُ وَاسِعٌ عَلِيمٌ 268 ) [البقرة:267 - 268]

Ma’ana : “Yaku waxanda ku ka bada gaskiya ku ciyar daga daxaxan abubuwan da kuka tsururuta da abin da muka fitar muku da cikin qasa, kada ku nufi mummuna ku ciyar daga cikinsa, alhali ku ba za ku karve shi ba idan an baku, sai da rintse idanu, ku sani lallai Allah mawadaci ne abin yabo. (Ku sani) Shaixan yana muku alqawarin talauci da rowa (idan kun bayar da abin da kuke da shi) Allah kuwa yana muku alqawarin gafara da falala. Allah mai yalwa ne kuma masani”. (Albaqra : 267 ).